Farmaki kan 'yan Boko Haram a Sambisa
February 19, 2015Talla
Mai magana da yuwun rundunar sojin Manjo Janar Chris Olukolade ya ce hare-haren da suka kai ta sama sun yi nasara matuka musamman ma a dajin na Sambisa idan kungiyar ke da sansanoni.
A 'yan kwanakin da suka gabata sojin na Najeriya sun ce sun hallaka 'yan kungiyar kimanin 300 a samamen da suka kai garururwa da dama inda suka karbe iko da su daidai lokacin da takwarorinsu da ke yakar kungiyar a Chadi da Kamaru da Nijar su ma suke bada labarin samun nasara a yakin da aka daura da Boko Haram din.