1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dangantaka ta yi tsami tsakanin Turkiyya da Girka

August 26, 2020

Kungiyar tarayayar Turai ta EU za ta tattauna kan wata tashin-tashina da ta kunno kai tsakanin Turkiyya da kasar Girka a kan tekun Bahar Rum.

https://p.dw.com/p/3hYWx
Deutschland Berlin | Treffen der EU-Verteidigungsminister
Hoto: Reuters/A. Schmidt

Ministocin kungiyar tarayyar Turai EU sun kudiri aniyar shiga tsakani, bayan da wata kiki-kaka ta kunno kai tsakanin Turkiyya da kasar Girka kan tekun Bahar Rum. An sanya ranar Alhamis mai zuwa domin tattauna yadda za a kawo karshen ta da jijiyoyin wayar.

Tuni dai shugaban Turkiyya Recep Tayyib Erdogan a ranar Larabar nan ya murza gashin baki, inda ya ce babu wanda za su daga wa kafa kan batun tekun, saboda mallakinsu ne kuma a shirye suke wajen daukar ko wane irin mataki da ya dace kama tun daga na siyasa har zuwa na soji.

A nata bangaren ministar tsaron Jamus Annegret Kramp-Karrenbauer ta Jamus ta fara duba yadda za a warware bakin zaren lamarin, inda ta ce shugabar gwamnatin Jamus Angela Markel ta shirya ganawa da shugaba Erdogan a Juma'a mai zuwa ta wayar tarho.