Nijar zabe cikin annobar corona
January 15, 2021Talla
Hukumar zabe dai mai zaman kanta tare da hadin gwiwar likitoci ta dauki matakai musamman ma dangane da halin da ake ciki na cutar Coronavirus mai saurin yaduwa a tsakanin al’umma, inda a wurare da dama hukumar ta dauki matakan da idan an yi amfani da su za a kai ga samun kariya. Da yake magana kan wannan batu mai magana da yawun hukumar zaben kasar ta Nijar CENI Malam Wada Nafiou, bayan ya isar da godiyar hukumar zaben ga yan Nijar da suka fito dafifi suka yi zabe, da kuma wadanda suka kama zabukan suka gudana, ya yi kira ga jama’a da su kiyaye matakan kariya na corona a lokacin zabe. Wannan batu na zabe da corona shi ne shirin Darasin rayuwa ya duba idan ana son karin bayyani daga kasa za a iya sauraron sauti.