1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tusk ya gargadi Turan kan dangantaka da Amirka

Abdullahi Tanko Bala
June 27, 2018

Yayin da Kungiyar tarayyar Turai EU ke shirin gudanar da taron koli a wannan makon shugabar kungiyar Donald Tusk ya ja hankalin shugabanin kungiyar kan tabarbarewar dangataka da Amirka

https://p.dw.com/p/30RQV
Luxemburg - Donald Tusk bei Pressekonferenz zum post-Brexit in Sennigen
Hoto: Getty Images/AFP/E. Dunand

Shugaban hukumar tarayyar Turai Donald Tusk ya ja hankalin shugabannin kasashen kungiyar tarayyar cewa su yi shirin fuskantar yanayi mafi muni a dangantakar kungiyar tarayyar Turai da Amirka.

Ya baiyana hakan ne a wata wasika da ya aike wa shugabannin kasashen Turan wadanda za su halarci taron kolin kungiyar da zai gudana a ranaikun Alhamis da Juma’a.

Tusk yace manufofin Trump na kara cin karo da akidun Kungiyar tarayyar Turai.

Batun ‘yan gudun hijira da na tattalin arziki su ne za su kasance kan gaba a jadawalin taron.