China ta bada tallafi don yaki da Ebola
October 20, 2014Talla
Shirin samar da Abincin na Duniya WFP ya bayyana a ranar Litinin dinann cewa; wadannan kudade za a tura su zuwa kasashen Laberiya da Saliyo da Guinea inda Cutar ta Ebola tafi kamari.
Wannan cuta dai a wadannan kasashe ta sanya manoma da dama kauracewa gonakinsu da dabbobinsu ga hauhawar farashin kayan abinci da ma kawo tarnaki ga shirin jigilar kayan abinci daga yanki zuwa yanki.
Wannan kudi ya kuma zama wani bangare na irin tallafin wannan kasa ta China bayan da a baya ta tura maaikata da kayayyakin kula da lafiya ga wadannan kasashe uku.
China ta kasance kasa ta biyu me karfin tattalin arziki da ta bada tallafi mafi girma cikin tallafin kasashen duniya a yaki da wannan cuta ta Ebola.