1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Boko Haram ta kashe sojoji 48

Abdul-raheem Hassan
September 3, 2018

An samu karin wasu gawarwakin sojojin Najeriya 17, bayan wani hari da mayakan Boko Haram suka kaddamar a sansaninsu da ke Zari a jihar Borno kan iyaka da Nijar wanda ya lamshe rayuka 30.

https://p.dw.com/p/34DFZ
Kamerun Symbolbild Soldaten im Norden ARCHIV
Hoto: Getty Images/AFP/R. Kaze

Rahotannin farko sun ce mayakan mayakan Boko haram sun kashe sojoji 30 a loakcin da kungiyarsu ta yi wa sojojin kofar rago a wani yanki da ke jihar Borno mai iyaka da Nijar a ranar Alhamis da ta gabata. A yanzu dai adadin sojojin 48 mayakan suka kashe, yayin da wasu rahotanni ke cewa an halaka 'yan Boko Haram da dama.

Wata sanarwa da rundunar tsaron Najeriyar ta fitar bayan harin, na cewa dakarun sun yi musanyar wuta da mayakan na Boko Haram. Sannan ta musanta yawan sojojin da Boko Haran ta yi ikirarin halakawa.

Wannan ba shi ne karon farko da kungiyar Boko Haram ke kaddamar da hare-hare kan sansanin sojojin Najeriyar ba, a daidai lokacin da gwamnatin kasar ke ikirarin karya lagon kungiyar da ke barazana ga rayuwar jami'an tsaro da fararen hula.

Sai dai yayin zantawa da kamfanin dillancin labaran Najeriyar NAN kakakin rundunar sojin kasar ya musanta rahotannin da ke cewa mayakan sun kashe sojoji 48.