1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta kai hari a Kamaru

December 5, 2020

Rahotannin da ke fitowa daga Kamaru, sun tabbatar da wani hari da mayakan Boko Haram suka kai yankin arewa mai nisa mai makwabtaka da Najeriya.

https://p.dw.com/p/3mG9f
Kampf gegen Boko Haram Nigeria
Hoto: picture-alliance/dpa/Ngala Chimtom

Kamar dai yadda bayanai suka tabbatar, harin da aka kaddamar a garin Assighassia, ya yi sanadin mutuwar akalla fararen hula uku da ma jikkatar wasu uku, a cewar Mahamat Chetima Abba, wani basaraken gargajiya a yankin Mozogo.

An dai yi zargin mayakan na Boko Haram sun fitio ne daga Najeriya, suka kuma afka wa mutanen ba-zata.

Wata majiya daga jami'an 'yan sanda da ba ta so a bayyana sunanta ba, ta tabbatar da faruwar lamarin.

Cikin 'yan watannin nan dai hare-hare daga mayan Boko Haram bangaren Al-Barnawi da ke jagorantar kungiyar ISWAP na kara tsanani a Najeriya da ma kasashe makwabtanta.