Najeriya: Boko Haram an bar baya da kura
July 30, 2019Kungiyar Boko Haram ta shafe tsawon shekaru 10 tana kai hare-haren ta'addanci a Najeriya ciki har a fadar gwamnatin tarayyar dake a Abuja. Rikicin da ya kara ta'azzara al'amurra na rayuwa da walwala dan Adam a yankin Arewa maso gabashin Najeriya, ya salwantar da rayukan jama'a dubu 100, sai dai a kokarin da gwamnatin Najeriya ke yi don yakar 'yan kungiyar, har yanzu akwai sauran jan aiki a gaba wajen kawo karshen rikicin.
Wannan lamarin ya sa kara saka sahkku a zukatan jama'a da ke yiwa yaki da kungiyar Boko Haram kallon wankin hula na son kai gwamnatin ta tarayyar Najeriya dare.
A fira da DW Hausa kakakin fadar gwamnatin Najeriya Garba Shehu ya bayyana cewa duk da hare-haren da ake samu na kungiyar sojojin kasar da ke bakin daga sun kusa kawo karshen tarzomar, a yayin da gefe daya kungiyoyin kare hakin bani Adama irinsu Amnesty International ke cewa jami'an tsaro na cin zarafin jama'a da sunan yaki da kungiyar Boko Haram.