1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Blinken: Za mu ci gaba da tallafa wa tsaro a Najeriya

Zainab Mohammed Abubakar MAB
November 18, 2021

Matsalar tsaro da Najeriya ke fama a ita da taimakon raya kasa na daga cikin batutuwan da suka mamaye ziyarar aiki da sakataren harkokin wajen Amirka Antony Blinken ke yi a Abuja babban birnin kasar.

https://p.dw.com/p/43Cet
Strategischer Dialog zwischen USA und Ukraine
Hoto: Leah Millis/AP/Reuters/dpa/picture alliance

Sakataren harkokin kasashen ketare na Amirka Antony Blinken ya bayyana cewa sun sanya hannu kan yarjejeniyar shirin tallafin raya kasashe da Tarayyar Najeriya. Blinken ya bayyana hakan ne jim kadan bayan ganawarasa da shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari yayin ziyarar da yake a yanzu haka a wasu kasashen nahiyar Afirka.

A cewarsa dai yarjejeniyar da suka sanya wa hannu tare da ministan harkokin waje na Najeriyar Geoffrey Onyeama za ta lashe zunzurutun kudi har dalar Amirkan biliyan biyu da miliyan 17. Ya kara da cewa Amirka za ta ci gaba da tallafa wa harkar tsaron Najeriyar da ke ci gaba da tabarbarewa.

A cewar mahkuntan Najeriyar dai, Blinken ya kai ziyara Najeriyar da ke zaman kasa mafi yawan al'umma a Afirka ne, domin tattauna batun tsaron cikin gida da kuma na yankin Sahel da ma batun yiwuwar Amirkan ta ba da taimakon da sojoji da bayanan sirri ga Najeriyar, a yakin da take da 'yan ta'adda.