1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yarima Ben Salmane ya yi tir da kisan Khashoggi

Gazali Abdou Tasawa
October 24, 2018

Yarima mai jiran gado na kasar Saudiyya Mohammed ben Salmane ya bayyana kisan dan jaridar nan Jamal Khashoggi da cewa wani babban abin kyama ne.

https://p.dw.com/p/378zQ
Saudi Arabien - Türkei l Saudischer Kronprinz Mohammed bin Salman und der türkische Präsident Erdogan
Hoto: picture-alliance/AP Photo/Presidency Press Service

Ya sanar da hakan ne a wannan Laraba a gaban taron zuba jari da ke gudana a yanzu haka a birnin Riyadh. Wannan dai shi ne karo na farko da yarima ben Salmane ya yi tsokaci kan wannan lamari tun bayan kisan dan jaridar a karamn ofishin jakadancin Saudiyya da ke a birnin Istanbul na Turkiyya a ranar biyu ga wannan wata na Oktoba. 

Sai dai kuma yariman ya bayyana cewa wannan hadari ba zai shafi huldar kasarsa da Turkiyya ba hasali ma za su yi aiki tare domin gano mutanen da suka aikata wannan danyen aiki domin gurfanar da su a gaban kuliya, kuma shari'a za ta yi aikinta

Da ma dai fadar Shugaban kasar ta Turkiyya ta sanar a wannan laraba cewa Shugaba Erdogan ya tattauna ta wayar tarho da Yarima Mohammed ben Salmane kan hanyoyin da ya kamata su bi wajen gano mutanen da suka aikata wannan danyen aiki.