"Bautar da 'yan Afirka da aka yi babban laifi ne" Mahama
March 25, 2026
Talla
Shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama daya daga cikin masu goyon bayan kungiyar tarayyar Afirka ta AU kan neman a biya Afirka diyyar bautar da aka yi musu, ya ziyarci hedikwatar Majalisar Dinkin Duniya don yada wannan da'awa.
Kudurin, kamar yadda ya shaida wa Majalisar Dinkin Duniya a ranar Talata, "ya ba wa Afirka dama a matsayin al'ummar duniya baki daya mu ba da shaida kan halin da ake ciki na sama da mutane miliyan 12.5 wadanda aka sace fatansu da mafarki da makomarsu tsawon shekaru 400."
Da yake kiranta da "kariya daga mantuwa," Mahama ya dauki niyyar yunkurin siyasa na baya-bayan nan a Amurka na haramta littatafai kan wannan batu domin "hana koyar da dalibai gaskiyar abin da ya faru a kan bauta da wariyar launin fata."