1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Arangama a tsakanin tsagerun yakin sa kai a kasar Somalia

May 11, 2006
https://p.dw.com/p/Buyn

Sojin sa kai na musulmai da kawancen madugan yaki a Somalia na ci gana da dauki ba dadi da juna, a kokarin da suke na kwace babban birnin kasar wato Magadishu.

Wannan dauki ba dadin dai na faruwa ne duk kuwa da yarjejeniyar tsagaitawa da bude wuta da aka cimma a tsakanin bangarorin biyu a jiya laraba.

Rahotanni da suka iso mana na nuni da cewa ya zuwa yanzu sojin sa kann musulmin na rike ne da kashi 80 cikin dari na birnin na Magadishu.

A dai dauki ba dadin daya faru a jiya laraba, an tabbatar da cewa mutane 13 ne suka rugamu gidan gaskiya, wasu kuma da dama suka jikkata.