1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana dakon sakamakon zaben Najeriya

Binta Aliyu Zurmi
February 27, 2023

A Najeriya a yau aka shiga rana ta biyu ta tattara sakamakon zaben shugaban kasa da na 'yan majalisun tarayya da ya gudana a karshen mako.

https://p.dw.com/p/4O0ki
Mahmood Yakubu
Hoto: Emmanuel Osodi/imago images

Hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta ce tana sa ran karban sakamakon daga jihohi da dama a wannan rana ta Litinin kuma ta sha alwashin sanar da sakamakon da zarar ta kammala karbarsa.

A jiya Lahadi ne aka sa ran hukumar za ta sanar da sakamakon sai dai jihar Ekiti ce daya tilo da ta aike da sakamakon nata a shalkwatar tattara shi.

Jinkirin fidda wannan sakamakon dai ya fara saka shakku a zukatan al'ummar kasar, kasancewar ikirarin da hukumar ta INEC ta yi tun da farko na fitar da sakamakon ba tare da bata lokaci ba.

Wannan zaben da ya gudana a ranar Asabar din da ta gabata na zama mai zafi tun bayan da kasar ta koma kan tafarkin mulkin dimukradiyya.

A daya hannu a jihar Legas wasu bata gari sun afka wa hukumar zabe a yayin da ma'aikatanta ke tsaka da kidayar kuri'u.