1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana cigaba da tashe-tashen hankula a Iraki

Mohammad Nasiru AwalMay 17, 2016

Mutane da dama sun mutu a wasu tagwayen hare-hare a wata unguwar 'yan Shi'a da ke birnin Bagadaza.

https://p.dw.com/p/1IpDZ
Irak Bombenanschlag in Bagdad - Distrikt Sadr City
Hoto: Reuters/K. al Mousily

Fiye da mutane 44 ne aka hallaka a wasu tagwayen hare-hare da a Iraki. Alkalumman da mahukunta suka bayar na cewa akalla mutane 90 kuma sun samu raunuka a hare-haren guda biyu da aka kai a unguwar Al-Shaab inda akasari 'yan Shi'a ke zaune da ke a arewacin Bagadaza babban birnin Iraki. Wani mai magana da yawun ma'aikatar cikin gida ya ce daga cikin wadanda suka kai harin kunar bakin waken har da mace guda. A kwanakin da suka wuce dai an fuskanci munanan hare-haren a Iraki wanda kungiyar IS mai da'awar kafa daular Islama ta dauki alhakin kaiwa.