1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Pakistan ta kare kanta game da hari a Kashmir

Zulaiha Abubakar
May 2, 2019

Hukumar tsaro ta Majalisar Dinkin Duniya ta kakabawa Masood Azhar jagoran kungiyar Jaish-i-Mohammed dake Pakistan takunkumi bayan da kungiyar ta sanar da daukan alhakin harin daya afku a yankin kashmir.

https://p.dw.com/p/3HnFl
Masood Azhar
Hoto: picture-alliance / dpa

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Pakistan Mohammed Faisal ne ya tabbatar da hakan yayin wata ganawar gaggawa da ya yi da 'yan jarida a Islamabad babban birnin kasar, ya kuma kara da cewar yanzu haka kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ta dakatar da kudaden Azhar da kuma haramta masa yin tafiye-tafiye. Wannan mataki dai na zaman nasara a bangaren Indiya wacce ta jima tana rokon Majalisar Dinkin Duniya ta kawo mata agaji game da harin da ya kara tsamin dangantakar kasashen biyu kan yankin na Kashmir. Pakistan dai ta bayyana cewar har yanzu bincike bai tabbatar da cewar kungiyar da Azhar ke jagoranta ce ta kai wannan hari ba.