1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai harin bam a Chadi

August 14, 2019

Wani harin bam ya yi sanadin asarar rayuka da kuma jikkatar wasu da dama a yankin da ya hada kasar da kasashe makwabta da suka hada da Najeriya da Nijar da kuma Kamaru.

https://p.dw.com/p/3NtQ0
Doppelanschlag in Tschad
Hoto: Reuters/M. Ngarmbassa

Rahotannin da ke fitowa daga N'Djamena babban birnin kasar Chadin na cewa wata 'yar kunar bakin wake ce ta kaddamar da harin da ya hallaka mutum shida ciki har da wani jami'in soja guda. 

Lamarin wanda ya faru a gundumar Kaiga-Kindjiria, ya kuma jikkata wasu mutanen da dama a cewar wata majiyar da ta fi son a sakaye sunanta.

Babu dai wata kungiyar da ta dauki alhakin harin da aka kaddamar da safiyar wannan Laraba, sai dai ana danganta shi da aika-aikar mayakan Boko Haram.

Yankin Kaiga-Kindjiria dai, yanki ne na tafkin Chadi da ya hada kasashen Najeriya da Nijar da Kamaru da kuma Chadin.   

Akalla hare-hare 10 ne mayakan tarzomar Boko Haram suka kaddamar a Chadi daga bara i zuwa halin da ake ciki.