1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An ceto ma'aikatan jami'ar Abuja

November 5, 2021

Hukumomin tsaro a tarayyar Najeriya sun ce sun yi nasarar ceto mutum 6 da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a jami'ar Abuja a wannan makon.

https://p.dw.com/p/42dSY
Nigeria entführte deutsche Archäologen wieder frei
Hoto: picture alliance/AP Photo/L. Oyekanmi

A ranar Talatar da ta gabata ce wasu 'yan bindiga suka yi garkuwa da wasu ma'aikatan jami'ar 4 da yaransu 2.  Kakakin rundunar 'yan sandan birnin Abuja Josephine Ader Anipr ta ce wadanda aka ceto sun sake ganawa da iyalansu.

A shekarun baya-bayan nan mussaman a arewacin Najeriya 'yan bindiga na garkuwa da gomman dalibai a makarantu don neman kudin fansa tare da kaddamar da munanan hare-hare a kauyuka.

Ci gaba da samun matsalolin tsaro a Arewa maso yammacin kasar da ma matsalar Boko Haram na tsawon shekaru 12 a Arewa maso gabashin kasar na jefa shakku kan makomar tsaron kasar da ta fi yawan al'umma a nahiyar Afirka.