Amurka za ta tura dakarunta 200 Najeriya don horas da sojoji
February 11, 2026
Mai magana da yawun hedikwatar rundunar sojin Najeriya, Manjo Janar Samaila Uba, ya tabbatar wa da kamfanin dillancin labaran AFP cewa shirye-shirye sun kammala na tarbar sojojin Amurka a Najeriya, duk dai a kokarin murkushe 'yan ta'addan da ke ci gaba da kashe fararen hula musamman a shiyyar arewacin kasar. To sai dai Janar Uba ya ce sojojin Amurkan ba za su shiga fagen daga ba, kawai za su bada horo ne ga sojojin Najeriya kan yaki da ta'addanci.
Karin bayani:Amurka ta kai hari kan 'yan ta'adda a Najeriya
Jaridar Wall Street Journal ce ta fara wallafa labarin zuwan sojojin Amurka akalla 200 Najeriya. Abuja dai na fuskantar matsin lamba daga Washington tun bayan zargin da Donald Trump ya yi cewa na ana kashe Kiristoci a kasar, wanda hakan ya haifar da rudani da kuma martani daban-daban daga ciki da wajen Najeriya.