1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zargi na yawaita kan Faransa game da Haftar

Zulaiha Abubakar
April 19, 2019

Faransa ta yi watsi da zargin da ma'aikatar harkokin cikin gida a Libiya ta yi mata na taimakon Khalifa Haftar wanda rundunar sojojinsa ta kaddamar da wani hari da nufin karbe birnin Tripoli babban birnin kasar.

https://p.dw.com/p/3H4C2
Emmanuel Macron, Fayez al-Sarraj und Khalifa Haftar
Hoto: picture-alliance/C. Liewig

Ma'aikatar cikin gidan Libiya ta sanar da dakatar da harkokin diplomasiyya tsakaninta da Faransa jim kadan bayan bayyana takaici game da rawar da Faransa take tawaka a rikicin da ya hana Libiya zama lafiya. Sai dai ana ta bangaren Faransa ta kara jaddada amincewa da gwamnatin  Firaminista Fayed al-Sarraj a matsayin jogora a Libiyan da kuma matakin sulhunta bangarorin da suka hana warware rikicin siyasar kasar da Majalisar Dinkin Duniya take yi a yanzu.

A wani sabon labarin kuma Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa cikin wannan wata na Afirilu mutane 205 ne suka rasa ransu a Libiya sakamakon rikicin bangarorin da ke yaki da juna lamarin da ya sanya ta tura kwararru a harkar lafiya don yi wa wadanda suka jikkata magani