Zanga zangar ma'aikata a Faransa
September 7, 2010Gwamnatin shugaba Nikola Sarkozy na Faransa, na shirin fuskantar zanga- zanga mafi girma ta ƙungiyoyin ƙwodago da ke shirin bazuwa yau a kan tituna, domin yin watsi da wata doka da ke shirin yin gyaran fuska ga tsarin kundin ma´aikatan ƙasar, mussamman batun ritaya .
Yan ƙwodagon waɗanda su ka ce zasu tattara kamar mutun miliyan biyu a zanga- zangar,
su na adawa ne da dokar da ke yin ƙari ga shekarun yin ritaya a ƙasar, wanda gwamnatin ta ke son ta mayar da shi daga shekaru 60 zuwa 62 kafin nan da shekara ta 2018.
Wannan zanga zanga wacce ita ce ta ukku da za a yi ,ta zo ne a daidai lokacin da Majalisar ɗokoki ta ƙasar ke fara mahawara akan dokar, wanda gwamnatin ke son a amince da ita a cikin watan Oktoba mai zuwa , wanda kuma bisa ga dukan alamu za ta fuskanci ƙalubale na jam'iyyun gurguzu na adawa.
Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Yahuza Sadissu Madobi