Za a yi bincike kan Cutar Ebola a Kwango
October 15, 2018Talla
Kwararrun za su isa Kwangon ne kan batun a Larabar da ke tafe don tababatar da girman barazanar da ta halaka mutum 135 a arewacin yankin Kivu daga watan Agusta zuwa yau.
Cutukan da ake bayyana su a matsayin matsalolin gaggawa dai su ne wadanda aka hakikance cewa suna iya ratsa iyakoki cikin hanzari, da kuma ke bukatar matakin kasashen duniya a gaggauce.
A shekara ta 2014 ma an bayyana Ebolar a wannan matsayin lokacin da ta halaka dubban rayuka a wasu kasashen Afirka ta Yamma kamar yadda aka bayyana cutar Zika a shekara ta 2016.