1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Habakar yawan jam'iyyun siyasa a Najeriya

June 21, 2018

'Yan watanni kafin babban zaben Najeriya na shekarar da ke tafe ta 2019 hukumar zabe mai zaman kanta ta INEC ta ce tana sa ran sama da jam'iyyu 100 za su kasance a cikin takardar zabe.

https://p.dw.com/p/302Rx
Schild in einem Wahllokal in Nigeria
Hoto: DW/T. Mösch

Ya zuwa yanzu dai akwai jam'iyyu dai dai har 68 da ke fatan taka rawa a cikin zaben tarrayar najeriya na watan Fabrairun shekarar badi. To sai dai kuma sama 136 ne dai ke layi kuma ke jiran samun rijistar kuri'a  a wani abun da ke shirin kafa tarihi na yawan jam'iyyu a cikin fagen siyasar Najeriya.

Nigeria Wahlen 2011 Bild 2
Hoto: DW/Gänsler

Ko bayan nan dai a fadar hukumar INEC din ana sa ran karin masu kada kuri'ar ya zuwa mutane kusan miliyan 80 daga 60 din da suka shiga cikin shirin a shekarar 2015.

Tuni dai yawan jam'iyyun ya fara tada hankali cikin kasar inda ilimin zaben ke da karanci sannan kuma mutuwa ko yin rai a cikinsa ke kara yawa.

Parlamentswahl 2011 in Kano State Nigeria
Hoto: DW

Dr Umar Kari dai na zaman wani mai sharhi a cikin harkoki na siyasa ta kasar, kuma a fadarsa ko bayan rudani ga alamomin jam'iyyun ana kuma iya fuskantar bacin kuri'u yayin zaben da yan kasar ke yi wa kallo da idanu na basira. Kuma a fadar Malam Aliyu Bello dake zaman kakaki na hukumar zaben, INEC tana tunanin samo hanyar tunkarar lamuran da a cewar sa ke tafiya a bisa dokoki na kasa.