1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan adawar Masar sun ce an yi magudi a kuri'ar raba gardama

December 15, 2012

Gamayyar 'yan adawar Siriya sun nuna rashin amincewarsu da yadda aka kada kuri'ar raba gardamar kan daftarin kudin tsarin mulkin kasar wanda aka gudanar da ita a wannan Asabar.

https://p.dw.com/p/173Gm
People checking their names in the voting lists. 15.12.2012, Heliopolis Copyright: DW/A. Hamdy
Verfassungsreferendum in ÄgyptenHoto: DW/A. Hamdy

'Yan adawar dai sun ce jam'iyyar 'yan uwa Musulmi ta shugaba Muhammad Mursi ta tafka magudi, baya ga yin amfani da kuri'un da ke bude da kuma yin amfani da wani alkali wajen hana wasu mabiya addinin kirista kada kuri'unsu a wata mazaba da ke birnin Alkahira.

Gabannin wannan kuri'a ta raba gardama dai, an yi ta zanga-zanga da kuma tada jijiyar wuya tsakanin mabiya jami'iyyar 'yan uwa Musulmi wadda ke mulkin kasar da kuma 'yan adawa wanda ba sa goyon bayan gudanar da jefa kuri'ar ta raba gardama kan sabon daftarin kundin tsarin mulkin kasar.

Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : Saleh Umar Saleh