1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yan adawa a Kenya sun bukaci a gudanar da zabe kafin lokacin sa

November 24, 2005
https://p.dw.com/p/BvJf

Yan adawa na kasar Kenya sun bukaci shugaba Mwai Kibaki daya shirya gudanar da zabe na gama gari kafin lokacin da aka tsara a can baya wato shekara ta 2007.

Wannan dai kira daga bangaren yan adawar yazo ne kwana daya bayan shugaba Kibaki ya sauke dukkannin jami´an majalisar zartarwar gwamnatin tasa, a sakamakon kaye daya sha a lokacin zaben raba gardama akan sabon kundin tsarin mulki na kasar.

A cikin wata takarda da jam´iyyun suka aikewa yan jaridu sun shaidar da cewa sakamakon zaben raba gardamar na nuni a fili cewa da yawa daga cikin alummar kasar sun dawo daga rakiyar gwamnatin ta Kibaki.

Idan dai za a iya tunawa da yawa daga cikin alummar kasar ta Kenya sun kada kuriun su na kin amincewa da wannan sabon kundin tsarin mulkin a ranar litinin din nan data gabata, wanda hakan ke a matsayin wani babban koma baya ga shugaba Mwai Kibaki a siyasan ce.

Rahotanni dai sun nunar da cewa wannan zabe na raba gardama akan sabon daftarin tsarin mulkin da alama ka iya kawo rarrabuwar kawuna a tsakanin kabilun kasar.