1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taba Ka Lashe: Azumi a arewacin Najeriya

Mohammad Nasiru Awal AH
April 27, 2021

A yayin da kwanakin azumin watan Ramadan ke wucewa sannu a hankali, ana ci-gaba da kwalla zafi a yankunan arewacin Najeriya, wanda hakan ke zaman kalubale ga masu ibadar.

https://p.dw.com/p/3sdeh
Nigeria Ramadan
Hoto: picture-alliance/AP Photo/S. Maikatanga

To ko baya ga yanayin zafin wani abin da ke ci wa Musulmin tuwo a kwarya shi ne karancin na gwamna masu gidan rana ga kuma matsalar rashin tsaro musamman a shiyyar arewa maso gabashin Najeriya. A duk shekara dai gwamnati na ba da taimako don saukaka radadin kunci da masu karamin karfi daga cikin masu azumin kan samu kansu a ciki. Yankin arewa maso gabashin Najeriya dai na fama da matsaloli na rashin tsaro, ko a 'yan kwanakin nan ma masu tada kayar baya sun kai hare-hare a wurare dabam-dabam a arewacin Najeriya. Wannan ya kara jefa yanayin azumin musamman irin hada-hada da aka saba yi lokacin azumi cikin rashin tabbas. Bugo da kari bayan wannan matsala ga kuma matsaloli na rashin kudi a hannun jama'a