1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugabannin kasashe da dama za su hallara a taron MDD

September 19, 2025

Rikicin Isra'ila da yankin Falasdinu zai kankane taron kasashen duniya na bana da za a yi a birnin New Yorka na Amurka, inda shugabannin kasashe da dama za su halarta. Sai dai Amurka ta hana shugaban Falasdinawa dama.

https://p.dw.com/p/50n5k
Zauren taron Majalisar Dinkin Duniya na birnin New York
Zauren taron Majalisar Dinkin Duniya na birnin New YorkHoto: Michael M. Santiago/Getty Images

Sama da shugabannin kasashe 140 ne za su hallara a birnin New York cikin makon gobe domin taron shekara-shekara na Majalisar Dinkin Duniya.

Matsalar jinkai da ta addabi yankin Falasdinu za ta kasance a kan gaba a tattaunawar, shekaru biyu bayan kaddamar da farmakin Isra'ila a Zirin Gaza, wanda ya samo asali daga mummunan harin kungiyar Hamas na ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Shugaba guda da ba zai halarci taron a Zahiri ba shi ne shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas, wanda Amurka ta hana biza tare da wadansu jami'ansa.

A karo na musamman, babban zauren ya kada kuri'a a ranar Juma'a domin bai wa Abbas damar yin jawabi ta hanyar bidiyo, yayin da jakadan Falasɗinu zai wakilce shi a cikin dakin taron.