A cikin shirin bayan labaran duniya akwai rahoton kan kaddamar da matatar man fetur ta farko mai zaman kanta da aka yi a Najeriya da rahoto kan yadda ake zargin 'yan siyasar Nijar da rasa alkibla a daidai lokacin da zaben shugaban kasar ke kara karatowa. Muna kuma dauke da halin da ake ciki dangane zaben shugaban kasa na Burkina Faso da kuma halin tsaro a yankin Tigray na Habasha.