A cikin shirin bayan a labaran duniya za a ji cewa a wani rahotonta da take wallafa wa a shekara-shekara kungiyar Welthungerhilfe ta Jamus ta ce Nijar na ci gaba da kasancewa daya daga cikin kasashen Afirka da matsalar 'yunwa ke addaba, a yayin da a Najeriya kuwa wani taro ne aka gudanar na kasa da kasa kan hanyoyin sulhunta rigingimu a kasashen yankin Sahel.