Muna amfani da "Cookies" domin inganta abubuwan da muke wallafawa a intanet. Za ku iya samun karin bayani a kundin kare bayananmu.
A cikin shirin bayan kun sha Labaran Duniya, muna tafe da rahoto kan yadda tashin nakiyoyi ke kara jefa rayuwar al'umma cikin tasku da ma asarar rayukan a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.
Kungiyoyin agaji na nuna damuwa game da komar da wasu 'yan Najeriya da suka tsere wa rikici gidajensu na asali a jihar Borno, bayan kwashe lokaci a Jamhuriyar Nijar.
Kungiyar tarayyar Turai ta bayyana bukatar kara yawan makamashin iskar gas da take saye daga Najeiya sakamakon kutsen Rasha a Ukraine da ya sanya nahiyar Turan neman hanyar cike gibin iskar gas da take saya daga Rasha.
A daidai lokacin da matsalolin tsaro ke kara ta'azzara a Najeriya, rundunar sojin kasar ta yi shelar kashe mayakan ISWAP fiye da 70 a yankin Tafkin Chadi mai iyaka da Jamhuriyar Nijar.
Wani rahoton bincike da kungiyar agajin kasa da kasa ta fitar ya nunar da cewa mutane sama da miliyan 27 sun fada matsalar yunwa a kasashen Afirka ta Yamma musamman Jamhuriyar Nijar da Najeriya da Burkina Faso da Mali.