1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rashin bin doka da oda a Libiya

October 23, 2013

Kungiyar NATO za ta ba wa sojojin Libiya horo na musamman domin tabbatar da tsaro a cikin gida da kuma kan iyakokinta, a wani mataki na magance kwararar bakin haure.

https://p.dw.com/p/1A4yw
Members of the security forces are seen outside the appeals court in Tripoli during the pre-trial hearing of ex-intelligence chief Abdullah Senussi and more than 20 former regime officials, accused of crimes during the 2011 revolt, on September 19, 2013. An AFP journalist said Senussi and more than 20 former regime officials appeared in court in the capital amid heavy security while Seif al-Islam Kadhafi, son of slain dictator Moamer Kadhafi, stood briefly in the dock before a judge adjourned his case in the western town of Zintan. AFP PHOTO / MAHMUD TURKIA (Photo credit should read MAHMUD TURKIA/AFP/Getty Images)
Hoto: M.Turkia/AFP/GettyImages

Shekaru biyu bayan gagarumar rawar da ta taka wajen rugurguza dakarun sojin Libiya, kungiyar NATO ta fara shirye-shiryen bada horo ga sabuwar rundunar sojin kasar, a daidai lokacin da matsalar tsaron kasar ta Libiya ta fara tsallakawa zuwa ketare.

A cikin wata sanarwa da ta gabatar a yayin taron jakadun kasashen kungiyar a birnin Brüssels, kungiyar ta kafa kwamati da zai tsara taswirar kan hanyar da za ta kai ga farfado da dakarun sojan kasar ta Libiya, don amsa rokon da Firaiministan kasar Ali Zaidani ya yi wa kungiyar, bayan da kasarsa ta fara zama tungar 'yan ta'addan da ke barazana ga tsaron duniya.

Ilyas Albaruni, kakakin Firaiministan na Libiya ya danganta matakin da kasar tasa ta dauka na sake gayyato NATO da wani mataki da ya zama na dole, don magance zaman kara zube da kasar ta yi shekaru biyu cikinsa.

"Batun tsaro, shi ne babban batun da muka sa gaba. Ba mu da niyar ba wa kungiyar NATO sansani a Libiya. Akwai yarjejeniyar cudeni in cudeka ta tsaro tsakaninmu da su, don haka muke fata za su sake taimaka mana don tunkarar wannan kalubale."

Sabon salon mulkin mallaka

Libya's Prime Minister Ali Zeidan (C) addresses a news conference after his release and arrival at the headquarters of the Prime Minister's Office in Tripoli October 10, 2013. Zeidan was seized and held for several hours on Thursday by former rebel militiamen angry at the weekend capture by U.S. special forces of a Libyan al Qaeda suspect in Tripoli. REUTERS/Ismail Zitouny (LIBYA - Tags: POLITICS CIVIL UNREST)
Firaminista Ali ZaidanHoto: Reuters

Wasu mayakan sa kai na kungiyoyin 'yan tawayen kasar, sun nuna adawarsu da wannan mataki da gwamnatin Ali Zaidanin ta dauka, suna masu cewa wannan mataki zai dawo da tsarin mulkin mallaka ne, da zai cusawa sojin kasar ta Libiya akidar kare bukatun kasashen iyayen gijinsu fiye da ba wa al'ummar kasar Libiya kariya.

"Mu mutanan garin Zawiya fafutukarmu ta kare hakkin 'yan kasa ne. Ba za mu lamunta da mayar Libiya ta zama sansanin dakarun kasashen ketare ba. Yanzu shin kakagidan da suka yi mana a rijiyoyinmu na man fetir, da kuma makudan kudaden da suke kwasa da sunan sake gina Libiya bai ishesu ba? Muna son ganin an gina sojojin Libiya kan akidar kishin kasa, da kaunar ilahirin mutanenta."

Demonstranten in Tripolis fordern die Auflösung der Milizen (Juli 2013) Bilder von Valerie Stocker, freie Autorin, aufgenommen von ihr.
Rikicin siyasa a Libiya na kara yin muniHoto: Valerie Stocker

Rashin bin doka da oda ya zama ruwan dare

Tun bayan karya gwamnatin Kanal Gaddafi shekaru biyun da suka gabata dai kasar ta Libiya take fama da matsalolin tsaro kama daga kisan dauki dai-dai da ake wa manyan jami'an tsaro da hafsoshin sojin kasar, gami da kai hare-hare kan ofisoshin kasashen Yamma, yadda a bara aka kone jakadan Amirka a ofishin jakadancin kasarsa dake Libiya. Sannan a baya bayan nan wasu 'yan bindiga sun yi garkuwa da shi kansa Firaiminista Ali Zaidani.

Kamar yadda masharhanta ke gani, fakewar da 'yan tawayen kasar Mali da dakarun sojin Faransa suka tarwatsa a cikin kasar ta Libiya, da kuma tururuwar da bakin hauren dake neman tsallakawa zuwa Turai ke yi a kasar ta Libiya, na daga cikin dalilan da ke nuni da matukar bukatar samar da gogaggun dakarun soji a Libiyar don kiyaye iyakokinta da kasashe yadda ya kamata.

Mawallafi: Mahmud Yaya Azare
Edita: Mohammad Nasiru Awal