1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mali za ta karfafa hulda da Rasha

Suleiman Babayo LMJ
February 7, 2023

Rasha tana ci gaba da karfafa ikonta a kasashen Afirka inda ta yi alkawarin taimakon kasashen yankin Sahel na Afirka da ke fama da matsalolin tsaro.

https://p.dw.com/p/4NCfq
Ministan harkokin wajen Rasha Sergey Lavrov
Sergey Lavrov ministan harkokin wajen RashaHoto: Russian Foreign Ministry Press Service/AP/picture alliance

Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergei Lavrov a wannan Talata ya bayyana cewa kasarsa za ta taimaki kasashen yankin Sahel na Afirka da suke fama da matsalolin tsaro na kungiyoyin jihadi. Lavrov ya fadi haka yayin ziyarar da ya kai birnin Bamako na kasar Mali da ke yankin yammacin Afirka. Ministan ya ce Rasha za ta taimakin kasashen domin shawo kan matsalolin da suke ciki.

A shekara ta 2020 sojoji suka kwace madafun ikon Mali inda suka karkata hulda daga Faransa wadda ta yi wa kasar mulkin mallaka zuwa kasar Rasha. Tun shekara ta 2012 kasar ta Mali ke fama da matsalolin tsaro daga kungiyoyi tsgaeru masu dauke da makamai da masu ikirarin jihadi.