Harin ta'addanci ya halla soja biyu a Nijar
October 8, 2019Talla
Ma'aikatar cikin gidan Nijar ta tabbatar da mutuwar jama'ian tsaron kasar biyo bayan wani dauki ba dadi da suka yi tare da galaba kan maharan masu dauke da muggan makaman yaki.
Wannan shi ne karo na biyu da wasu da ake kyautata zaton mayakan jihadi ne ke kai farmaki a jihar ta Dogondoutchi mai makwaftaka da Najeriya inda a baya maharan suka kai hari a kauyen Bagaji, da yayi sanadiyar hallaka jamai'an gendarme biyu da wani farar hula daya a cikin watan Afrilun wannan shekrara.