Nakiyoyi sun tashi a Fatakwal, Nigeria | Labarai | DW | 20.04.2006
  1. Inhalt
  2. Navigation
  3. Weitere Inhalte
  4. Metanavigation
  5. Suche
  6. Choose from 30 Languages

Labarai

Nakiyoyi sun tashi a Fatakwal, Nigeria

Kungiyyar dake gwagwarmayar kwatowa yan yankin Niger Delta a tarayyar Nigeria yancin su, wato Mend, tace itace ta dana nakiyoyin da suka tashi a jikin wata mota da aka ajiye kusa da wani barikin soji dake birnin Fatakwal, babban birnin Jihar Rivers.

.Kungiyyar ta Mend ta fadi hakan ne a yau ,a cikin wani sako data aike izuwa yanar giza gizan sadarwa na duniya, wato Internet a turance.

Wannan dai kungiyya ta Mend data dade da yin kaurin suna wajen dauki ba dadi da jami´an tsaro a yankin na Niger Delta, ya zuwa yanzu bata fadi dalilin kai wannan hari ba.

Wannan mummunan aiki dai ya zuwa yanzu a cewar rahotanni yayi sanadiyyar rasuwar mutane biyu, wasu kuma kalilan sun jikkata