1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya ta soke rundunar SARS

Abdul-raheem Hassan MNA
October 11, 2020

Bayan jerin zanga-zanga daga kan cin zarafi da rundunar SARS ke yi wa farar hula, babban sufeton 'yan sanda Mohammed Adamu ya sanar da soke rundunar yaki da 'yan fashi da makami wato SARS nan take.

https://p.dw.com/p/3jlCQ
Symbolbild | Nigeria | SWAT
Hoto: AFP/Y. Chiba

Wannan mataki ya biyo bayan jerin zanga-zanga mai zafi daga fitattun 'yan kasar a ciki da waje da kuma shafukan sada zumunta na neman a soke rundunar kan zargin yadda suke kashe rayukan mutane da dama.

A shekarar 1992 ce gwamnatin Najeriya ta kirkiro da sashin SARS domin yaki da masu fashi a kasar, sai dai tun bayan nan an wa rundunar kallo tana fakewa da kaki tana cin zarafin al'umma, zargin da rundunar ta ce babu gaskiya a cikinsa. An dai samu wasu kungiyoyi da ke neman a wanke rundunar daga dukkannin zargi da suka da suke sha daga kudancin kasar.