1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Najeriya ta kubutar da daliban Kebbi daga hannun yan bindiga

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
November 26, 2025

Shugaban Najeriya Bola Tinubu, ya ce ta hanyar laluma suka ceto 'yan matan, ba tare da wata hatsaniya ba.

https://p.dw.com/p/54Gto
Jami'an tsaro da ke gadin makarantu a Najeriya
Hoto: Deeni Jibo/AP Photo/picture alliance

Fadar shugaban Najeriya ta tabbatar da kubutar da daliban nan 24 'yan mata, na makarantar sakandaren Maga a jihar Kebbi, wadanda 'yan bindiga suka yi garkuwa da su ranar 17 ga watan Nuwamba.

Kakakin shugaban Bayo Onanuga, ya ce ta hanyar laluma suka ceto 'yan matan, ba tare da wata hatsaniya ba.

Karin bayani:'Yan bindiga sun sake sace daliban Najeriya cikin mako guda

Shugaba Bola Tinubu ya alkawarta samar da karin jamai'an tsaro, domin magance afukuwar hakan a nan gaba, bayan da aka fuskanci hare-haren 'yan bindiga da ke garkuwa da mutane kwanan nan a jere, a sassa daban-daban na kasar.