1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya ta fasalta dokar hako man fetur

Binta Aliyu Zurmi
July 15, 2021

Majalisar dattijan Najeriya ta amince da fasalta dokar harkokin man fetur a kasar, inda za a fara bayar da kaso 3% na adadin kudaden shiga da kasar ta samu daga albarkatun mai zuwa ga yankunan da ake hako man.

https://p.dw.com/p/3wXSA
Nigeria Politik l Senat
Hoto: Getty Images/AFP/K. Sulaimon

A wannan Alhamis, majalisar dattijan Najeriya ta kada kuri'a amincewa da dokar sake fasalta harkokin man fetur din kasar, mataki da ke zama na karshe da suka yi aiki a kai a 'yan kwanakin bayan nan, bayan shafe shekaru da dama da kudirin ke a gabansu.

Guda daga cikin abin da sabuwar dokar za ta kunsa shi ne bai wa kaso 3 cikin dari na adadin kudaden shiga da kasar ta samu daga albarkatun mai zuwa ga yankunan da ake hakar man.

Majalisar wakilai za ta yi nata zama a kan wannan kudirin dokar kafin daga bisani a tura wa shugaban kasa Muhammadui Buhari da zai sa mata hannu ta zama doka.