Najeriya: Rikici a zaben Bayelsa da Kogi
November 16, 2019Wakilin DW da ke yankin Niger Delta Muhammad Bello ya shaida mana cewar an samu tsaikon wajen fara zaben a wasu sassan jihar yayin da a wasu wuraren ciki kuwa har da Yenagoa babban birnin jihar, an yi harbe-harbe da samun satar akwatuna, batun da ya kai ga dakatar da zaben a wasu wuraren.
Can a jihar Kogi inda takara ta fi zafi tsakanin jam'iyyar APC mai mulki da PDP da ke adawa ma dai an samu rahotanni na samun tashin hankali a wusu yankunan. Wakilinmu Ubale Musa da ke sanya idanu kan yadda lamura ke gudana a Kogi din ya ce an samu rahotanni na tada hankali da ma satar kuri'a a Lokoja, babban birnin jihar.
Tuni dai aka fara tattara sakamakon zaben daga matakin mazabu a jihohin na Bayelsa da Kogi kuma nan gaba ake sa ran mika shi ga kananan hukumomi kafin daga bisani a kai ga matakin jiha inda za a tattara sakamakon kana a bayyana wanda ya yi nasara a hukumance.