Najeriya: Sace-sacen jama'a yana kara tsamari
October 9, 2019Talla
An soma satar mutane domin karban kudin fansa a yankin Niger Delta shekara 15 da suka gabata inda ake garkuwa da ma'aikatan kanfanonin hakan manfetur, sai dai yanzu wannan matsala ta game kasa baki daya.
Duk da cewar wasu naganin batun na garkuwa da jama'an, bata rasa nasaba da matsanaicin talauci, hada da rashin aikin yi da ma shan miyagun kwayoyi da ke addabar al-umma.
Hukumomi dai na cewa suna kokarin don ganin sun sama wa matsalar ta satar mutane magani. Kakakin hukumar ta farin kya da ake kira Civil Defense, Chief Superintendent Suleiman Baba, ya tabbatar da faruwan wannan lamarin, da irin matakanda suke dauka a kai.