Najeriya: Magance rikicin manoma da makiyaya
June 5, 2026
Rikicin ya faro ne daga inda wasu makiyaya suka kai farmaki kan wasu manoma a kauyen Lanzai da ke karkashin karamar hukumar ta Darazo yayin da suke aikin zuba taki a gonakinsu.
Wannan shi ya fusata matasa daga garin na Lanzai suka je daukar fansa a kauyen Dosho inda fulanin suke da zama suka cinna wa gidaje wuta lamarin da ya kai ga asarar rayuka,
Da farko aka samu rashin mutune bakwai kafin daga bisani alkaluma suka gwada sha daya ne. Kan haka ne kuma gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Abdulkadir Muhammad y ace gwamnatinsa ba za ta lamunci hakan ba.
Tuni dai rundunar yan sandan jihar Bauchin ta aika da jami'anta zuwa garuruwan na Lanzai, Dabo da Dosho domin tabbatar da zaman lafiya a yankin kamar yadda kwamishinan yan sandan jihar Sani Omolori Aliyu ta bakin kakakin rundunar SP Nafi'u Habib.
Rundunar yan sandan jihar Bauchi ta ce jami'anta ba za su bar garuruwan da aka yi rikicin ba har sai komai ya koma daidai.