1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Jirgin ruwa ya nutse da fasinjoji a jihar Neja

Ramatu Garba Baba
May 26, 2021

A Najeriya ana cike da fargabar rasa rayuka da dama a sakamakon wani hadarin jirgin ruwa da ya rutsa da fasinjoji sama da dari a jihar Neja

https://p.dw.com/p/3u0RM
Fährunglücken im Kongo
Hoto: picture alliance / dpa

Fasinjoji kimanin dari da sittin jirgin ya dauko kafin ya nutse a tsakiyar ruwa bayan da aka ce jirgin ya dare gida biyu. Abdullahi Buhari Wara, wanda shi ne dagacin yankin Ngaski inda aka yi hadarin, ya ce kawo yanzu, mutum ashirin da biyu kadai aka yi nasarar ceto wa, an kuma gano gawar mutum guda, amma har yanzu ba su san inda saura, sama da dari suke ba.

Karin rahotanni na cewa, jirgin ya taso ne daga garin Minna da ke jihar ta Neja inda ya nufi jihar Kebbi da safiyar wannan Laraba, daga dai cikin fasinjojin sama da dari, akwai mata da yara kanana. Hadarin jirgin ruwa makamancin wannan, ana ci gaba da bincike da fatan gano sauran da ba a gani ba ya zuwa wannan lokacin.