Najeriya: Harin bindiga a Coci na jihar Anambara
August 6, 2017Talla
Hukumomi yankin sun sanar cewa mutane 11 ne suka mutu, sannan wasu 18 suka samu raunuka. Sai dai kuma wasu alkaluman da ba na hukumomin ba na cewa wadanda suka mutun sun kai kimanin 50 zuwa sama da 100. Gwamnatin jihar ta Anambra ta tattara kimanin likitoci 50 don bada kulawar gaggawa kan wadanda harbin 'yan bindigar ya rutsa da su, tare da alkawarin daukan nauyinsu. Sai dai kuma wasu da suka dubi lamarin na nuni da cewa harin na da nasaba da rashin jituwar da ke tsakanin wasu 'yan uwan juna kan batu da ya shafi harkokin gudanar da wannan coci.