1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabbin tsare-tsare a gidajen yarin Najeriya

Uwais Abubakar Idris AH
August 15, 2019

Gwamnatin Najeriya ta sanar da gagarumin sauyi a fannin kula da gudanar da gidajen yarin kasar, inda a sabon tsarin aka bullo da sabbin tsare-tsare da za su taimaka wajen gyara hallayen fursunonin.

https://p.dw.com/p/3NxxI
Wannan wani tsohon hoto ne a muka yi amfani da shi
Wannan wani tsohon hoto ne da muka yi amfani da shiHoto: Getty Images/AFP/S. Maina

Wadannan sauye-sauye da aka sanar a kan harkar kula da fursunonin a gidajen yarin kasar sun biyo bayan rattaba hannu a gyaran fuskar da aka yi wa dokar da ta kafa wannan hukuma da shugaba Muhammadu Buhari ya yi. Sauye-sauyen da suka hada da sanya fursunonin su yi aiki a cikin al’umma da kuma daurin talala dukka da nufin gyara  hallayensu.

 An dai dade ana koke a kan halin da gidajen yarin Najeriyar suka shiga inda a kan tsare fursunoni da nufin gyara hallayensu amma sai su fito cike da munana dabi’un da suka koya wadanda gara ma kafin tsaresu. To sai dai tuni ana fara nuna damuwa a kan batu na kayan aiki da za’a iya aiwatar da wadannan sauye-sauye.

Justiz Liberia
Hoto: Meredith Safer

A ‘yan shekarun nan dai an ga sauye-sauye a hukumar gidajen yarin Najeriyar da ta bullo da tsarin karatu ga fursunonin inda wasu suka kai ga kammala digiri na digigir watau karatun dokta, da wadanda suka koyin sana’oi iri dabam-dabam.