1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Filato na neman taimakon magance rikicin jahar

Abdullahi Maidawa Kurgwi RGB
June 27, 2018

Gwamnan Filato Simon Lalong, ya roki shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, da ya dauki matakai na shawo kan rikicin jahar kamar yadda ya fuskanci matsalar Boko Haram a jihohin arewa maso gabashin kasar,

https://p.dw.com/p/30OCR
Nigeria Angriff von Nomaden im Bundesstaat Plateau | Muhammadu Buhari, Präsident
Hoto: Reuters/Nigeria Presidency

Gwamna Lalong ya yi wannan kira ne a wata ganawa da shugaba Buhari ya yi da wakilan al'umomin Filato a yammacin jiya a Jos. Wakilan al'umomin Fulani da Berom, tare da shugabanin wasu kabilun jahar, sarakunan gargajiya da shugabanin addinai ne suka halarci zaman. Lalong a jawabinsa ya nuna damuwa kan irin halin da jahar Filato ke neman komawa.

Da ya ke mayar da martani, shugaba Buhari ya ce baya barci kan matsalar tsaro da tashe-tashen hankula da ke aukuwa a sassan kasar daban.

Shugaban rikon mulkin karamar hukumar Riyom, Emmanuel Danboyi Jugul, ya ce abinda ke haddasa rikici a jahar a duk lokacin da aka sami tashe-tashen hankula tsakanin kabilun Fulani da Berom matafiya dake bin hanya tsakanin Abuja zuwa Jos, kan shiga halin firgita sakamakon yadda wasu matasa kan tsare hanya suna cin zarafin su.

A wata ganawa da muka yi da shi kakakin rundunar da ke wanzar da zaman lafiya a jahar Filato Major Adamu Umar ya tabbatar da cewa, yanzu hankula sun soma kwanciya, inda jami'an tsaro ke zirga-zirga ta sama da kasa a kauyuka da a ka fi samun damuwa don tabbatar da doka da oda.