1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Najeriya: An soma bincike kan kisan 'yan #EndSARS

Ramatu Garba Baba
October 21, 2020

Gwamnatin jihar Legas ta kaddamar da bincike kan kisan masu zanga-zanga a yankin Lekki a daren ranar Talata. Rahotanni na cewa mutum kusan ashirin ne suka mutu bayan da jami'an soja suka bude musu wuta.

https://p.dw.com/p/3kDc7
Nigeria Ikeja | End Sars Proteste | Demonstranten
Hoto: Pius Utomi EkpeiAFP/Getty Images

Gwamnatin jihar Legas a Najeriya ta ce za ta kaddamar da bincike a game da kisan masu zanga- zanga a sakamakon bude musu wuta da aka ce sojoji sun yi a jiya Talata. Al'ummar Najeriya sun kwana da jimami a sakamakon hargitsin da ya biyo bayan zuwan sojojin a dandalin da ke Lekki. Batun da ya janyo suka da kuma alhini a ciki da ma wajen kasar. 

Kungiyar Amnesty International ta ce akwai rahotanni da ke tabbatar da kisan masu zanga-zangar a sanadiyar harbe-harben sojoji sai dai kawo yanzu rundunar sojin kasar ba ta ce komai ba. Hargitsin dai ya biyo bayan bijirewa dokar gwamnatin jihar da masu zanga-zangar suka yi na hana fita bayan da aka kona wani ofishin yan sanda.