Najeriya: An dakatar da shirin RUGA
July 3, 2019Talla
Gwamnatin ta Najeriya ta ce ta dau matakin dakatar da shirin saboda irin cece-kucen da ake yi a kai. A wani zama da kwamitin nan na wadata kasar da abinci ya yi a Abuja, mukaddashin kwamitin kuma gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu ya ce, Shugaban kasar Muhammadu Buhari ne ya bada umarnin dakatar da shirin na RUGA. Ya bukaci da a sake duba shi da nufin yi masa gyaran da ya kamata, ta yadda wandada za su amfana da shirin za su ci moriyarsa sosai, sannan a kawar da duk wani abu daga cikinsa da ka iya jawo fitina a kasar.