1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD ta bukaci bai wa fararen hula kafa a El-Fasher na Sudan

October 27, 2025

Sakamakon halin da fararen hula ke ciki a yankin Darfur na Sudan, Majalisar Dinkin Dunixya ta bukaci da a ba su kafar ficewa bayan kwace iko da yankin da mayakan RSF suka yi a karshen mako.

https://p.dw.com/p/52cTG
Sudan El Fasher 2025 | Wata yarinya tana dafa abinci a wani sansanin 'yan gudun hijira a yankin Darfur.
Hoto: UNICEF/Xinhua/picture alliance

Majalisar Dinkin Duniya ta yi kiran da a bude hanyoyi ga fararen hula da suka makale ko suke tserewa daga birnin El-Fasher na kasar Sudan, bayan dakarun RSF suka bayyana sun karbe iko da birnin a jiya Lahadi.

Shugaban sashen agajin jin kai na Majalisar Dinkin Duniya, Tom Fletcher, ya bayyana damuwarsa kan rahotannin kashe-kashen fararen hula a El-Fasher, birnin da shi kadai ne ya rage a yammacin Darfur ba tare da fadawa hannun mayakan RSF ba kafin yanzu.

Mista Fletcher ya ce dubban fararen hula sun makale cikin yunwa da fargaba, ba kuma tare da samun abinci ko kula da lafiya da tsaro ba.

Rahotanni dai sun nuna cewa sama da mutane dubu 260, rabinsu kananan yara ne suka makale a cikin birnin na El-Fasher ba tare da wata hanyar samun abinci ko taimako ba.