Majalisar Dinkin Duniya ta ce Buhari ya taka doka
February 11, 2019Talla
Wani mai magana da yawun Majalisar Dinkin Duniyar Diego Garcia Sayan ya ce dokar kasa da kasa da ta yi daidai da ta kare hakin bil Adama ta ce ba za a iya cire alkali ba a kan aikinsa idan ba wata babbar tabargaza ya yi ba, ko ya nuna gazawa a game da aikinsa. Sannan ya ce duk wani hukumci mai kama da irin wannan, sai majalisar alkalai ko wata hukuma ta musammun kan iya daukar mataki a kai.