Martani kan kamen da jami'an tsaron Najeriya suka yi
July 1, 2014A Najeriya sanarwar da hedikwatar tsaron ƙasar ta fitar na samun kame wa ni ɗan kasuwa da ta ce shi ne ya kitsa sace ‘yan mata nan sama da 200 'yan makarantar na garin Chibok a jihar Borno. Ya sanya maida martani da ma tambayar ko kame shi ya kwantar da hankalin masu fafutukar ganin an ceto ‘yan mata daga hannun Ƙungiyar Boko Haram.
Sanarwar da jami'an tsaron Najeriyar ta bayar, na kame mutumin da ta bayyana shi a matsayin wanda ke da hannu dumu-dumu a sace 'yan matan na garin Chibok da ma wasu hare-haren da aka kai na zama matakin farko da sojojin suke fatan zai iya taimakan gano bakin zaren matsalar.
Mutumin wanda da suka bayyana shi da suna Babuji Ya'ari wanda suka danganta shi da cewar dan leƙen asiri ne ga Ƙungiyar ta Boko Haram da ke faffatawa da gwamnatin Najeriyar yanzu haka ana tsare da shi.
Da ƙasa za a iya sauraron wannan rahoto
Mawallafi: Uwais Abubakar Idris
Edita: Pinado Abdu Waba