1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ko mecece makomar kasar Mali?

Lateefa Mustapha Ja'afar
May 27, 2021

Sojojin da suka kwace mulki a hannun gwamnatin  rikon kwarya ta Mali, sun sallami shugaban Bah N'Daw da Firaminista Moctar Ouane jim kadan bayan da suka yi marabus daga mukamansu a barikin soja na Kati.

https://p.dw.com/p/3u43n
Mali Massenkundgebung in Bamako
Cikin watan Agustan bara ma dai, sojoji sun karbe mulki daga Ibrahim Boubacar KeitaHoto: picture-alliance/AP Photo

Shugaban Mali na rikon kwarya Bah Ndaw da firaministansa Moctar Ouane sun sanar da ajiye aikin nasu ne, kwanaki biyu bayan da soji suka yi musu juyin mulki kana suka tsaresu. Majalisar Dinkin Duniya da ma ECOWAS da sauran kasashen duniya, sun bukaci a sakesu kana a mayar da kasar kan turba ta mulkin dimukuradiyya.

Sai dai duk da haka sabanin yadda mutane suka fito yin zanga-zangar murna da kifar da gwamnatin Ibrahim Boubacar Keita a watan Agustan bara, a wannan karo jama'a da dama sun fito nuna kyama ga matakin kwace mulkin da sojojin suka sake yi. 

Ana iya cewa dai, a yanzu babu tabbas kan halin da Malin za ta tsinci kanta a ciki, ganin cewa an yi juyin mulkine ne kasa da shekara guda da kifar da gwamnatin tsohon shugaban kasar Ibrahim Boubacar Keita tare da kafa gwanatin wucin gadi. An dai amince gwamnatin za ta mika mulki ga farar hula daga bisani. Sai dai kuma da wannan sabon juyin mulki, abin tambayar shi ne: Ina Mali ta dosa?