1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Salon rayuwaTurai

Matsalar yawan yara cikin bakin haure

Pieper Oliver | Mouhamadou Awal Balarabe SB
October 30, 2025

Kungiyoyin da ke ceto a teku na gargadi kan yawan yara da matasa 'yan Afirka da ke yunkurin ratsa Bahar Rum domin zuwa Turai ta barauniyar hanya. Wannan ya sanya tekun zama daya daga cikin hanyoyin hijira mafi hadari.

https://p.dw.com/p/52qS6
Bakin huaren da aka ceto daga cikin teku
Bakin huaren da aka ceto daga cikin tekuHoto: SOS Humanity

 

Wani saurayi dan shekara 15 da ya fito daga Guinea Conakry, na daga cikin wadanda kungiyar SOS Humanity ta ceto a tekun Bahar Rum, a lokacin da yake yunkurin shiga Turai ba tare da rakiya wani mutum da ya mallaki hankalin kansa ba.

Bayanin halin da ake ciki

Harsasai bayan harbin da masu gadin tekun Libiya suka yi
Harsasai bayan harbin da masu gadin tekun Libiya suka yiHoto: Max Cavallari/SOS Mediterranee/AP Photo/picture alliance

Ita wannan kungiya mai zaman kanta da ke da mazauna a birnin Berlin na Jamus, ta shafe shekaru goma tana ceto bakin haure da ke neman nutsewa a teku. Saboda haka ne ta ja hankali kan yawan yara da matasa da ke shiga kwale-kwalen da ke cike da mutane daga Libya ko Tunisiya, inda ta ce kusan kashi daya cikin biyar na wadanda aka ceto yara kanana ne.

Esther, da ta ce a sakaye sunanta, kwararriyar masaniyar ilimin halayyar dan adam, ta yi aikin sa kai a matsayin jami'ar kula da lafiyar kwakwalwa a jirgin ceto na Humanity 1 a watan Nuwamba da Disamba 2024. Ta ba da labarin cewa kwale-kwale shida dauke da mutane 347 suka ceto su, kuma daga cikinsu akwai yara kanana 43, galibi matasa marasa rakiya a yanaqyi na raunin jiki da tunani.

Bakin huaren da aka ceto daga cikin teku
Bakin huaren da aka ceto daga cikin tekuHoto: SOS Humanity

Libiya tana cikin hanyoyin masu hadari

Masu karancin cikin sahekaru na cikin mummunan hali a sansanonin da ke tsugunar da su a Libiya, kasar da ke fuskantar suka mai tsanani kan take hakkin bakin haure ta hanyar cin zarafi da azabtarwa, da fataucinsu. Sai dai, idan yara da matasan da ke neman tsallakawa Turai suka samu damar tserewa daga sansanonin, suna fuskantar hadarin rasa rayukansu.

Till Rummenhohl na kungiyar SOS
Till Rummenhohl na kungiyar SOSHoto: SOS Humanity

Kiyasin da Asusun Yara ta UNICEF ta yi daga watan Afrilun 2025, ya nunar da cewar kimanin yara da matasan Afirka 3,500 sun mutu ko sun bace a cikin shekaru goma da suka gabata yayin da suke kokarin isa Italiya ta hanyar tsallaka Bahar Rum. Wannan yana nufin cewar yaro daya na mutuwa ko yana bacewa a kowace rana a tsawon shekaru goman da suka gabata. Saboda haka ne kungiyar SOS Humanity ta yi kira da a kawo karshen hadin gwiwar Kungiyar Tarayyar Turai da Libya da Tunisiya.

Lanna Idriss ta kungiyar SOS
Lanna Idriss ta kungiyar SOSHoto: David Ausserhofer

Rushewar USAID yana da mummunan sakamako

Matsalar da yara da matasa da ke neman zuwa Turai ta barauniyar hanya na iya ta'azzara a nan gaba, in ji Lanna Idriss, Shugaba na SOS Children's Villages, bayan da gwamnatin Amurka a karkashin Shugaba Donald Trump ta rusa hukumar ba da agajin ta USAID.